DAGA SAIFULLAH M. KABIR
Bislmillahir Rahmanir Rahim
Allahumma Salli Ala Muhammad Wa Ahli Muhammad
Sheik as-Sudduk (Allah ya kara masa rahma) ya fitar a cikin littafinsa
mai suna “Uyun al-akhbar ar-Ridha (a.s)” da isnadinsa da ya kare da
Amirul-mu’uminin Ali bin Abi Dalib (a.s) ya ce:
Manzon Allah (s.a.w.a) ya yi mana huduba a wata rana (a watan Ramadan), inda yake cewa:
“Ya ku mutane! Lallai hakika watan Allah mai albarka ya zo muku
(tattare) da rahama da gafara. Watan da shi ne mafificin dukkan watanni a
wajen Allah, ranakunsa kuma su ne mafifitan raneku, sa’o’insa kuma sune
mafifitan sa’o’i.
Shi wata ne da aka kira ku zuwa bakuncin
Allah a cikin shi, aka kuma sanya ku cikin ma’abota karimcin Allah a
cikin shi. Numfashinku a cikin shi ibada ne, haka ayyukanku a cikin shi
karbabbu ne, kuma addu’o’inku a cikin shi abin amsawa ne; don haka ku
roki Allah Ubangijinku da gasgatattun niyyoyi da tsarkakan zuciya kan
cewa Ya sa ku sami dacewa da azumtar sa (watan) da karatun littafinSa
(Allah), domin lallai tababbe (na hakika) shi ne wanda ya rasa gafarar
Allah a wannan wata mai girma.
Ku tuna da kishirwar lahira ta
hanyar yunwa da kishirwanku a cikinshi. Kuyi sadaka ga matalautanku da
miskinanku, ku girmama dattawanku, kuma ku tausayawa kanananku, ku kuma
sadar da zumuninku. Ku kame harsunanku kuma ku kau da kai daga abubuwan
da ba ya halatta idanuwanku su kalla da abubuwan da ba ya halatta
kunnuwanku su ji.
Ku tausayawa marayun mutane, ku ma sai a
tausaya marayunku. Ku tuba zuwa ga Allah daga zunubanku, ku daga
hannuwanku zuwa gare Shi da addu’a a lokutan sallolinku, domin (lokutan
sallolin) ne mafifitan lokutan da Allah Madaukaki ke kallon bayinSa da
rahama a cikin su, Ya ke sauraron su idan suka gana da shi, Ya kuma amsa
musu idan suka roke Shi.
Ya ku mutane! Lallai numfashinku
jingina ne ga ayyukanku, don haka ku fitar da su (numfashin) da
istigfarinku. Haka bayayyakinku sun nauyaya da ayyukanku, to ku sassauta
musu da tsawaita sujjadunku. Ku sani cewa Allah Madaukaki Ya rantse da
daukakarSa cewa ba zai azabtar da masu sallah da masu sujjada ba. Kuma
ba zai raunana su da wuta a ranar da mutane za su tsaya gaban (Allah)
Ubangijin talikai ba.
Ya ku mutane! Wanda ya bude bakin mai
azumi mumini a wannan wata, to da hakan yana da ladan (wanda) ya ‘yanta
bawa a wajen Allah da gafararta abin da ya gabata na zunubbansa”.
Sai aka ce ya Manzon Allah, ba kowannen mu ne zai iya haka ba. Sai Manzo (s.a.w.a) ya ce:
“Ku kaucewa wuta ko da da tsagin dabino ne! ku kaucewa wuta ko dad a kurbin ruwa ne!!”
“Ya ku mutane! Wanda ya kyautata halayyarsa a wannan wata zai ketare
siradi a ranar da kafafu ke zamewa; kuma wanda ya sassauta ga wadanda ya
mallaka Allah Zai saukaka masa hisabinsa; kuma wanda ya kame sharrinsa a
cikin shi (wannan wata) Allah Zai kame fushinSa daga gare shi a ranar
da zai hadu da Shi, kuma wanda ya kyautatawa maraya a cikin shi Allah
zai karrama shi a ranar haduwar su. Haka wanda ya sadar da zumuncinsa a
cikin shi Allah zai sadar da rahmarSa gare shi a ranar haduwar su; wanda
kuwa ya yanke zumuncinsa Allah zai yanke rahmarSa gare shi ranar da zai
hadu da shi.
Wanda ya yi nafilar salla a cikin shi Allah Zai
rubuta mishi barranta daga wuta. Wanda ya sauke nauyin farilla a cikin
shi kuwa yana da ladan wanda ya sauke nauyin farillai saba’in a wasu
watannin da ba shi (Ramadan) din ba; wanda ya yawaita yi mini sati a
cikin shi Allah zai nauyaya mishi ma’aunin ayyukansa a ranar da ma’aunan
ayyuka ba su da nauyi; wanda ya yi tilawar aya daya daga al-Kur’ani
kuwa yana da ladan wanda ya sauke al-Kur’ani a wani wata da ba shi ba.
Ya ku mutane! Lallai an bude kofofin Aljanna, don haka ku roki
Ubangijinku da kar Ya rufe su gare ku; kuma an rufe kofofin wuta, to ku
roki Ubangijin ku kar ya bude su gare ku; haka an daure shedanu, don
haka ku roki Allah kar su sami iko a kan ku.”
Sai Amirul-Muminin Ali (a.s) ya mike ya ce: “Ya Manzon Allah, mene ne mafifiin ayyuka a wannan wata?”
Sai Manzon Allah (s.a.w.a) ya amsa masa da cewa: “Ya kai Baban Hasan!
mafificin ayyuka a wannan wata shi ne tsentseni (kame kai) daga abubuwan
da Allah Ya haramta.”
ALLAH YA SA MUNA CIKIN WADANDA ALLAH KE GAFARTAMA A WANNAN WATAN

No comments:
Post a Comment